Posts

Showing posts from May, 2021

ABUN NEMA YASAMU GA MUSULMIN DUNIYA.

  Ministan Harkokin Wajen Iran Jawad Zarif ya bayyana cewa, a shirye suke da su kusanci Saudiyya. A tattaunawar da Zarif ya yi da 'yan jaridu a Dimashk Babban Birnin Siriya ya bayyana cewa, "A koyaushe a shirye muke da mu kulla kyakkyawar alaka da Saudiyya". A watan da ya gabata gwamnatin Iraki ta bayyana shiga tsakanin Saudiyya da Iran inda ake kuma ci gaba da tattaunawa a tsakanin bangarorin 2. A baya Yariman Saudiyya Salman bin Abdulaziz ya tattauna da wata tashar talabijin inda ya bayyana cewa, suna da sha'awar kulla kyakkyawar dangantaka da Iran. Ma'aikatar Harkokin Wajen Iran ta bayyana cewar, sun gamsu da jin dadin kalaman na Yarima bin Salman. Alakar kasashen 2 ta sakwarkwace a shekarar 2016 bayan da Saudiyya ta zartar da hukuncin kisa kan wani Malamin Shi'a Nimr Al-Nimri, kuma sakamakon martanin da Iran ta mayar da kaiwa jami'an diplomasiyyar Saudiyya hari a Tehran ya sanya lamarin ya kara munana tare da yanke huldar jakadanci a tsakaninsu.

ANYI ZANGA ZANGAR KIN JININ ISRA,ILA A TURKIYYA

A fadin kasar Turkiyya an gudanar da zanga-zangar la'antar Isra'ila kan yadda take kai hare-haren ta'addanci kan Falasdinawa a Gabashin Kudus da kuma yunkurin korar Falasdinawa ta karfi da yaji daga unguwar Shaikh Jarrah a yankin. Kungiyar Matasan Anatoliya ta jagoranci taruwar jama'a a gaban karamin ofishin jakadancin Isra'ila dake Istanbul inda aka karanta Alkur'ani Mai Tsarki a wajen. Masu zanga-zangar dauke da tutar Falasdin sun dinga cewa, "Mun sadaukar da rayukanmu da jininmu ga Aksa" da kuma "Allah Ya tsinewa Isra'ila". Shugaban Kungiyar a Istanbul Yunus Genc ya shaida cewa, Masallacin Aksa na da babban matsayi ga Musulmai. A garin Elazig ma kungiyar kwadago ta ma'aikatan gwamnati ta shirya zanga-zangar la'antar Isra'ila. An daga tutar Falasdin a jerin gwanon motocin da aka yi. Dubunnan jama'ar Malatya ma sun taru tare yin tofin Alla tsine ga Isra'ila sakamakon hare-haren da take kaiwa Falasdinawa, sun kuma nuna...

Press statement

 Press Statement For Immediate Release May 9, 2021 State of the Nation: A Call to President Muhammadu Buhari to the Stop the Bleeding and Take Action to End the carnage. #NigeriaBleeds Following its sharp increase of 43% in mass atrocities 2020, Nigeria has continued to experience a decline in security across the nation. In the first quarter of 2021(January to March), we recorded an all-time quarterly high of almost 2000 fatalities from mass atrocities incidents across the country. This week, across the 6 geopolitical zones, there were escalated combustions of violence resulting in even more deaths. In our last joint statement, we had issued in February 2021, we had catalogued the assortment of mass atrocities plaguing the country, in particular: The unending war in the North East with our troops often bearing the brunt of this government’s security failures. Gross injustices by President Buhari’s government against the Nigerian people such that peaceful protesters are threatened a...

AREWA AYAU

YAKI YANA NEMAN CINYE AREWA DA MUTANAN CIKIN TA Mu sani cewa abinda yake faruwa a Arewa na ta'addancin Boko Haram, Garkuwa da mutane, harin 'yan bindiga duka wannan salo ne na yaki a zamanance, ana yakar nahiyar Arewan Nigeria ta yanda wadanda ake yakar ba zasu ankara da wake yakar suba Sabon salon yaki ne ake mana, manufar ita ce a yaki Arewa wajen karya mata tattalin arziki da neman ilmi, a ruguza mata tsarin tsaro, a kakaba mata talauci da rashin zaman lafiya, a yayata barna da kuma yawaita mutuwa cikin al'ummah, ta yadda mutane za su kasance kowa ta kansa yake Sannan kuma a tabbatar da cewa lalatattun mutane cikin Arewa sune za'a basu damar zama  shugabanni a Gwamnati, Malaman Addini a mayar da su 'yan barandan gwamnati, masu fadin gaskiya kuma a kassara su A hana noma da kiwo wajen tabbatar da rashin tsaro a Arewa, a yada makamai ko ina, a kona  kasuwanni lokaci zuwa lokaci, a hana karatu da wanzuwar ilimi a Arewa, a mayar da mutane 'yan gudun hijira, a may...