Ali Khamenei ya amince da kasancewar Ibrahim Reisi a matsayin sabon shugaban kasar Iran a makon da ya gabata, wanda ya baiwa Ibrahim Reisi damar fara aiki bayan bukukuwan da aka gudanar. Daga bisani kuma bikin rantsarwar da aka gudanar a majalisar Shura ya baiwa shugaban cikekken damar kama ragnar mulkin kasar. A lokacin yakin neman zabe, zabebben shugaban ya yi alkawarin bunkasa hulda da kasashen dake makwabtaka da lran tare da kuma inganta fannonin kasar da dama. Bayan lashe zabe a jawabin da ya yi da manema labarai ya yi alkawarin daidaito da Saudiyya. Haka kuma ana cigaba da wannan daidaitawa da shiga tsakanin lraki. A sabanin haka anga kuma yadda mayaka yan shi'a suna ayyuka a Siriya da lraki. Abubuwa kamar hare-hare da killacewar da kungiyoyin da Iran ke marawa baya a Daraa ke yi da kuma ayyukan dakarun kare juyin juya halin lran suka fara na tono rami a birnin Palmyra na nuna cewa tasirin Iran a Siriya zai karu a mulkin Ibrahim Reisi. Ci gaban da Rasha za ta yi na zamanantar...
Kungiyar Taliban ta bayyana cewa za ta tabbatar kowanne dan kasar Afghanistan ya samu damar walwala tana mai cewa ba ta bukatar abokan gaba. A taron manema da take gudanar yanzu haka, mai magana da yawun kungiyar Zabihullah Mujahid, wanda ya bayyana a gaban 'yan jarida a karon farko tun bayan da suka kwace iko, ya ce sun 'yantar da kasar "bayana shekaru 20 na fafutika kuma mun kori 'yan kasashen waje". "Wannan lokaci ne na alfahari," in ji shi. "Muna son tabbatar da ganin Afghanistan ba ta sake tsunduma cikin yaki ba. Mun yafe wa dukkan mutanen da suka yake mu. Gaba ta zo karshe, " a cewarsa Mujahid
Comments
Post a Comment